8 Faburairu 2022 - 14:08
Ana ci Gaba Da Gudanar Da Zaga-zangar Adawa Da Gwamnatin Soji A Sudan

Tun bayan da sojoji suka yi juyin mulki a kasar Sudan a watan Oktoban a ake ci gaba da zanga-zanga a manyan biranen kasar, da hakan ya tilastawa fira ministan kasar Abdallah Hamdok yin murabus amma duk da haka masu zanga zanga sun ci gaba da kasancewa a kan titunan har sai kun kawo karshen mulkin soji a kasar.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA -Ko a jiya ma dubun dubatan mutane ne suka yi zanga zangar a birnin Khartum domin kin amincewa da juyin mulki da sojoji suka yi, inda sojoji suka yi amfani da harsashi mai raid a haki mai sa hawaye wajen tarwatsasu , lamarin da yayi sanadiyar jikkata adadi mai yawa,

Masu zanga-zangar sun sha Alwashin ci gaba da hawa kan tituna har sai sun ga bayan mulkin soji a kasar, dubban mutane dake fitowa zanga zangar na daga cikin abin da ke kara daukar hankali da kuma kara mata armashi a idon duniya.

342/